languageIcon
search
search
Zikirin Dare Da Yini Zikirin Dare Da Yini ( Adadinsu 4 Babuka )

1 Sau Da Yawa

brightness_1

اللَّهُ لَا إِلَهَ إِلَّا هُوَ الْحَيُّ الْقَيُّومُ لَا تَأْخُذُهُ سِنَةٌ وَلَا نَوْمٌ لَهُ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ مَنْ ذَا الَّذِي يَشْفَعُ عِنْدَهُ إِلَّا بِإِذْنِهِ يَعْلَمُ مَا بَيْنَ أَيْدِيهِمْ وَمَا خَلْفَهُمْ وَلَا يُحِيطُونَ بِشَيْءٍ مِنْ عِلْمِهِ إِلَّا بِمَا شَاءَ وَسِعَ كُرْسِيُّهُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ وَلَا يَئُودُهُ حِفْظُهُمَا وَهُوَ الْعَلِيُّ الْعَظِيمُ

Sunna ne a karanta áyatul- kursiyyi  idan za a shiga bacci domin neman tsari daga Shaixanu har a wayi gari.

Hujja a kan wannan Sunna ita ce: Qissar Abu Huraira raliyallahu anhu da mutumin nan da yake satar kayan zakka, inda a cikin Hadisin Abu Hurairah raliyallahu anhu yake cewa: “Sai Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallam ya ce mani: “Me varawon da ka kama ya aikata jiya? Sai na ce: “Ya Manzon Allah! ya karantar da ni wasu kalmomi ne, da ya ce, idan ina karanta su zan sami rabo ga Allah. Sai kawai na sake shi. Sai Manzon Allah ya ce: “Waxanne kalmomi ne waxannan?  Sai na gaya masa cewa: “Ya gaya mani ne cewa: “Duk lokacin da ka yi shirin kwantawa bacci, to, ka karanta áyatul- kursiyyi tun daga farkonta har qarshe, wato: “Allahu lá iláha illá huwal- Hayyul- Qayyúmu….” Sa’annan kuma sabon Malamin ya qara da gaya mani cewa: “Idan ka karanta ta, za ka ci gaba da samun tsaro daga wurin Allah; wani Shaixani ba zai iya kusantar ka ba, har safiya ta waye. Babu abin day a kai alhairi muhimmanci ga waxannan matsara.” Sai Annabi sallallahu alaihi wa sallam ya ce mani: “Ko shakka babu, abin day a gaya maka xin nan gaskiya ne. sai dais hi a karan kansa maqaryaci ne. Ashe ba ka san wanda kake magana das hi ba tsawon kwana uku. Ko ka sani ya kai Abu Huraira.”  Sai na karva masa da cewa: “Ban sani ba ya Manzon Allah!” Sai ya ce: “Ai Shaixan ne.”  (Buhari:2311), Imamun- Nisa’i kuma ya sadar da danganen Hadisin a cikin:  as- Sunanul- Kubra:10795)

.......

1 Sau Da Yawa

brightness_1

اللَّهُمَّ رَبَّ السَّمَاوَاتِ وَرَبَّ الأَرْضِ وَرَبَّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ، رَبَّنَا وَرَبَّ كُلِّ شَيْءٍ، فَالِقَ الْحَبِّ وَالنَّوَى، وَمُنْزِلَ التَّوْرَاةِ وَالإِنْجِيلِ وَالْفُرْقَانِ، أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ كُلِّ شَيْءٍ أَنْتَ آخِذٌ بِنَاصِيَتِهِ، اللَّهُمَّ أَنْتَ الأَوَّلُ فَلَيْسَ قَبْلَكَ شَيْءٌ ، وَأَنْتَ الآخِرُ فَلَيْسَ بَعْدَكَ شَيْءٌ، وَأَنْتَ الظَّاهِرُ فَلَيْسَ فَوْقَكَ شَيْءٌ، وَأَنْتَ الْبَاطِنُ فَلَيْسَ دُونَكَ شَيْءٌ، اقْضِعَنَّا الدَّيْنَ وَأَغْنِنَا مِنَ الْفَقْرِ

“Alláhumma Rabbas- samáwáti, wa Rabbal- ardhi, wa Rabbal- arshil- azími. Rabbaná wa Rabba kulli shai’in, fáliqal habbi wan- nawá, wa munzilut- Tauráta wal- Injil wal- Furqán. Aúzu bika min sharri kulli shai’in anta Ákhizun bi násiyatihí. Alláhumma antal- Auwalu fa laisa qablaka shai’un, wa antal- Ákhiru fa laisa ba’adaka shai’un, wa antaz- Záhiru fa laisa fauqaka shai’un, wa antal- Báxinu fa laisa dúnaka shai’un, aqdhi annád- daina wa angina minal- faqri.” (Ya Allah! Ubangijin sammai da qassai, Ubangijin kuma al’arshi mai girma. Ubangijinmu, Ubangijin kuma dukan komai. Ya Mahaliccin qwaya iri, wanda ya saukar da Attaura, da Linjila, da Alqur’ani. Ina neman tsarinka daga sharrin duk wani abu da, jijiyar goshinsa take hannunka. Ya Ubangiji! Kai ne na farkon da babu wani abu a kafinsa, kai ne kuma na qarshen da babu wani a bayansa. Kai ne bayyanannen da babu wani abu birbishinka, kai ne kuma voyayyen da babu wani abu da ya yi maka iyaka. Ya Ubangiji! Ina roqon ka biya mana bashi, ka kuma yi mana maganin talauci da fatara.) [Muslimu:2713].

.......

100 Sau Da Yawa

brightness_1

سبحان الله (33)، الحمد لله (33)، الله أكبر (34) م

Yana daga cikin Sunna, idan mutum zai shiga bacci ya yi tasbihi ta hanyar karanta: “Subhánalláhi”  qafa 33. Sa’annan ya yi godiya ga Allah Maxaukakin Sarki ta hanyar karanta:  “Alhamdu lilláhi”  qafa 33. Sa’annan ya girmama Allah Maxaukakin Sarki ta hanyar karanta:“Alláhu Akbar”  qafa 34. Yin haka yana da falala mai girma, wadda ta haxa da samun cikakken kuzari a cikin jikinsa tsawon wannan rana.

Hujja a kan wannan Sunna ita ce, Hadisin Sayyadi Ali raliyallahu anhu, cewa, wata rana Sayyida Faximah raliyallahu anha ta qosa da  irin yadda dutsen niqa ya yi mata kanta a hannu. Sai ta tasar wa Annabi sallallahu alaihi wa sallam, don ta kai qara, amma ba ta same shi ba; sai Sayyida A’isha kawai ta iske, ta kuma labarta mata. Da Annabi sallallahu alaihi wa sallam ya dawo, sayyida A’isha ta gaya masa cewa, Faxima ta zo ba ya nan, ga kuma abin da ya kawo ta. Jin haka, in ji Sayyadi Ali, sai Annabi sallallahu alaihi wa sallam ya tasar wa gidanmu. Ko da ya iso mun shiga bacci. Mun yunqura haka, mu tashi, sai ya ce: “Ku yi kwancinku.”   Sai kuma ya shiga tsakanina da ita ya zauna, har na ji danshin qafarsa a qirjina. Sa’annan ya ce: “Ko kuna son in ba ku labarin abin da ya fi abin da kuka roqe ni zama alhairi? Duk lokacin da kuka shimfixa awazanku a kana shimfixar baccinku. To, ku  girmama Allah Maxaukakin Sarki ta hanyar karanta:“Alláhu Akbar”  qafa 34. Sa’annan ku yi tasbihi a gare shi, ta hanyar karanta: “Subhánalláhi”  qafa 33. Sa’annan ku yi godiya gare shi ta hanyar karanta:  “Alhamdu lilláhi”  qafa 33. Wannan shi ne mafi zama alhairi a gare ku bisa ga a ba ku xan aiki.”  (Buhari:3705/ Muslim:2727).

A cikin wata riwaya kuma aka ce, sai Sayyadi Ali raliyallahu anhu ya qara da cewa: “Tun daga wannan lokaci da na ji wannan magana daga bakin da ba ya qarya; na Annabi sallallahu alaihi wa sallam, ban tava kwantawa bacci ba tare da na karanta su ba.” Aka ce masa: Har daren da aka gwabza yaqin basasar Siffin? Ya karva da cewa: Tabba! Har shi.” (Buhari:5362/ Muslimu:2727).

.......

1 Sau Da Yawa

brightness_1

اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْلَمْتُ وَجْهِي إِلَيْكَ، وَفَوَّضْتُ أَمْرِي إِلَيْكَ، وَأَلْجَأْتُ ظَهْرِي إِلَيْكَ، رَغْبَةً وَرَهْبَةً إِلَيْكَ. لاَ مَلْجَأَ وَلاَ مَنْجَا مِنْكَ إِلاَّ إِلَيْكَ، آمَنْتُ بِكِتَابِكَ الَّذِي أَنْزَلْتَ، وَبِنَبِيِّكَ الَّذِي أَرْسَلْتَ

“Alláhumma aslamtu wajhí ilaika, wa fauwadtu amrí ilaika, wa alja’atu zahrí ilaika, ragbatan wa rahbatan ilaika. Lá malja’a walá manjá illá ilaika. Ámantu bi kitábikallází anzalta, wa bi Nabiyyikal- lazí arsalta.” (Ya Ubangiji! Na miqa fuska gare ka, na kuma damqa al’amarina hannunka, sa’annan na jingina bayana gare ka, ina mai kwaxayin rahama da fargaban azabarka. Babu wata mafaka ko wata matsera, sai zuwa gare ka. Na yi imani da littafinka wanda ka saukar, da Annabinka wanda ka aiko.) [Buhari:247/ Muslimu:2710]…. A qarshen Hadisin, Annabi sallallahu alaihi wa sallam ya ce: “Mutum ya yi qoqari wannan addu’a ta zama qarshen abin da zai furta a wannan rana. idan Allah ya karvi rayuwarsa a wannan dare, to, ya mutu a kan aqidar Musulunci.”  Imamu Muslimu kuma a cikin tasa riwaya, ya qara da cewa, Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallam ya qara da cewa: “Idan kuma ya wayi gari, to, ya wayi gari a cikin alhairi.”  

Wannan Hadisi kuma, ya zo da qarin bayani na wata Sunnar, wato: qoqarin ganin ba a qara furta wata kalima ba bayan wannan addu’a kafin a kwanta bacci. Yin haka kuma yana qunshe da wata barrar garavasa; idan an karvi rayuwar mutum a cikin wannan dare, to, ya mutu a kan aqida ta Musulunci; addinin Annabi brahima alaihissalamu, wanda bai tava yi wa Allah Maxaukakin Sarki kishiya ba. Idan kuma an wayi gari yana cikin rayayyu, to, zai sami yalwar arziki da wadata. Wannan addu’a, bakandamiya ce; ta haxa duk abin da waxanda suka gabace ta suka qunsa.

Akwai kuma wani qasaitaccen ‘zikiri’ wanda yake zama sanadin samun qasaitacciyar lada da fafa, wanda Allah Maxaukakin ya yi ni’imsarsa ga mutane. Zikiri, wanda ya kamata mai karatu ya lura da shi, shi ne zikirin nan ya zo a cikin Sahíhul- Buhari daga cikin Hadisan Sahaddad xan Aus raliyallahu anhu, daga Annabi sallallahu alaihi wa sallam, cewa: “Mafi girma da xaukakar kowane irin istigfari, shi ne mutum ya ce: “Alláhumma Anta Rabbí lá’iláha illá anta. Khalaqtaní, ana abduka, wa ana alá wa’adika mas’taxa’tu. Aúzu bika min sharri má sana’atu, abú’u laka bi ni’imatika, wa abú’u laka bi zanbí. Fagfir lí, fa innaú lá yagfiruz- zunúba illá anta.” (Ya Allah! Kai ne Ubangijina. Babu wani abin bauta da gaskiya sai kai. Kai ka halicce ni, ina nan kuma a kan alqawalin da na xauko tsakanina da kai, gwargwadon ikona. Ina neman tsarinka daga sharrin duk abin da na aikata. Ina godiya gare ka a kan ni’imar da ka yi mani, ina kuma kai qarar zunubaina zuwa gare ka. Ina roqon ka gafarta mani. Saboda babu wanda yake gafarta zunubai sai kai.) Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallam ya ce: “Duk wanda ya karanta wannan addu’a da rana yana mai imani da ita. To, idan ya mutu a wannan rana, kafin marece, yana daga cikin ‘yan Aljanna. Wanda kuma ya karanta da dareyana mai imani da ita. To, idan ya mutu kafin a wayi gari, yana daga cikin ‘yan Aljanna.”  (Buhari:6306).

.......

1 Sau Da Yawa

brightness_1

اللَّهُمَّ أَنْتَ رَبِّي لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ خَلَقْتَنِي وَأَنَا عَبْدُكَ وَأَنَا عَلَى عَهْدِكَ وَوَعْدِكَ مَا اسْتَطَعْتُ أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا صَنَعْتُ أَبُوءُ لَكَ بِنِعْمَتِكَ عَلَيَّ وَأَبُوءُ لَكَ بِذَنْبِي فَاغْفِرْ لِي فَإِنَّهُ لَا يَغْفِرُ الذُّنُوبَ إِلَّا أَنْتَ

Akwai kuma wani qasaitaccen ‘zikiri’ wanda yake zama sanadin samun qasaitacciyar lada da fafa, wanda Allah Maxaukakin ya yi ni’imsarsa ga mutane. Zikiri, wanda ya kamata mai karatu ya lura da shi, shi ne zikirin nan ya zo a cikin Sahíhul- Buhari daga cikin Hadisan Sahaddad xan Aus raliyallahu anhu, daga Annabi sallallahu alaihi wa sallam, cewa: “Mafi girma da xaukakar kowane irin istigfari, shi ne mutum ya ce: “Alláhumma Anta Rabbí lá’iláha illá anta. Khalaqtaní, ana abduka, wa ana alá wa’adika mas’taxa’tu. Aúzu bika min sharri má sana’atu, abú’u laka bi ni’imatika, wa abú’u laka bi zanbí. Fagfir lí, fa innaú lá yagfiruz- zunúba illá anta.” (Ya Allah! Kai ne Ubangijina. Babu wani abin bauta da gaskiya sai kai. Kai ka halicce ni, ina nan kuma a kan alqawalin da na xauko tsakanina da kai, gwargwadon ikona. Ina neman tsarinka daga sharrin duk abin da na aikata. Ina godiya gare ka a kan ni’imar da ka yi mani, ina kuma kai qarar zunubaina zuwa gare ka. Ina roqon ka gafarta mani. Saboda babu wanda yake gafarta zunubai sai kai.) Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallam ya ce: “Duk wanda ya karanta wannan addu’a da rana yana mai imani da ita. To, idan ya mutu a wannan rana, kafin marece, yana daga cikin ‘yan Aljanna. Wanda kuma ya karanta da dareyana mai imani da ita. To, idan ya mutu kafin a wayi gari, yana daga cikin ‘yan Aljanna.”  (Buhari:6306).

.......